Sai dai shi kansa kamfanin na Google yana kera manhajojin da agogunan zamani masu dauke fasahar tantance lafiyar jiki ke amfani da su, abinda ya sanya kungiyar kasashen Turai, bayyana damuwa kan cewar kamfanin na Google zai samu damar da ta zarce ka’ida a kasuwar fasahar sadarwa, wajen fin karfin sauran kamfanoni takwarorinsa, muddin ya mallaki rumbun fasahohin kamfanin Fitbit.

A halin yanzu hukumar gudanarwar kungiyar kasashen Turan EU na da wa’adin watanni 3, na gudanar da binciken tantance katafaren cinikin da Google ke shirin yi, wanda bayan kammala shi za ta tantance yiwuwar gindayawa kamfanin wasu ka’idoji don baiwa abokan hamayyarsa a kasuwar fasahar sadarwa kariya.


Kada ku manta kuyi sharing ga abokanku a social media domin suma su amfana